Dan kwallon kafan Nigeria Hadi bala ya Yankee jiki ya rasu ana tsaka da wasa da spai

Dan kwallon kafan Nigeria Hadi bala ya Yankee jiki ya rasu ana tsaka da wasa da spai

Mukaran ta wannan labarin da kyau

AKWAI ABIN BAN TAUSAYI A CIKIN

 

Wannan labarin wani yaro ne me kimanin shekara 5 Mahaifiyarsa ta Rasu, sai yaga K

kawai ya dai na ganinta sai ya tambayi babanshi yace: Baba ina mama taje?,

se baban yace: maman ka tana lahira, se yaro yace: yaushe zata dawo? se baban uayi shiru baice komai ba.

 

Wata rana yaron yana wasa da abokanshi

bayan angama wasa se kowa yace bari yaje

gida gurin maman shi se yaron yace shima

so yake idan ya girma ya samu kudi yaje Lahira don baban shi yace maman sa tana Lahira, se daya daga cikin Abokanensa yace: nima zaka je dani? se yaron yace Ehh.

 

Wata rana yaron yana makarantar islamiyya malamin su yana wa’azi yana cewa ‘duk wanda ya mutu idan yaje lahira bazai dawo ba’ se yaron ya daga hannu yace malam to idan mutun be dawo ba toh me yakeyi acan?.

 

Sai malamin yace: Lahira gurine inda ake hisabi ga Matattu kuma duk wanda ya mutu baya dawowa, Sai yaron yace: idan mutun ya mutu ina ake kaishi, se malam yace: Makabarta,

 

Sai yaron yace: Meyene Mutuwa? Se malamin yace: mutuwa tana nufin fitar Ruhi daga jikin dan Adam,

 

Sai yaro yace: Toh ina Ruhi yake ajikin dan

Adam? se malam yace kai yaro ka cika

tambaya dayawa, Je ka zauna,

 

Washe gari bayan sallar Asuba sai yaron yazo gurin babanshi yace ina kwana baba ka tashi lafiya? Baban yace lafiya qalau, se yaron yace baba Inada tambaya, se yace to inajin ka ɗana miye Tambayarka? Se yaron yace: baba Wai ina Ruhin mamana yake? Se baban yayi shiru…………. Can se baban yace: Yaro saurara in baka wani labari Mamanka ta Rasu, Rasuwa kuma idan akayita ba’a dawowa duk wanda aka zarewa Ruhi daga jikinsa bazai rayu ba, lokacin mamanka ne Yayi Shi Yasa Ta rasu, nima idan lokacina yayi Zan mutu na Barka!

 

Sai yaron yace: Toh baba Don ALLAH idan zaka mutu ka gayamun domin nima inaso Na mutu se In rakaka zuwa gurin mamana naji kewarta wllh baba,

 

Sai baban yayi shiru don yaga Alamar Yaronnan.Yanason Mamansa kuma yaga Alamar lallai yaron Yana bukatar ganin mamanshi, se babanshi yace je kashirya kazo muje zan kaika inda mamanka take yanzu, .

 

Sai yaro yaje yayi wanka Yaci kwalliya yana murna zeje gurin mamansa, Dasauri yazo gurin babanshi yace Baba Gani nashirya muje, se baban yakama Hannun yaron

suka fita suna ta tafiya har suka bar Gari

suka shiga daji, suka Isa makabarta, se baban ya nufi Qabarin maman wannan Yaron, Sai

baban yace; Yaro mamanka tana cikin wannan Qasar, Wannan qasar itace Qabari, kuma duk wanda ya mutu a ciki ake sakashi, kuma duk wanda ya mutu baya iya motsi baya iya komai, a haka za’a kawoshi

anan gurin kuma a binneshi baya iya yin

komai se ikon ALLAH, Se yaro ya fashe da

kuka ya fadi qasa yace: Mamana yanzu itace a cikin wannan Qasa?

 

Sai yace Toh baba wane laifi tayi da ALLAH ya kasheta? Se baban yace kowa haka ze mutu idan lokaci yayi,

 

Suna zaune se ga wasu mutane sunzo da Gawa za’a binneta a cikin Qabari se yaron ya Qura ido yaga duk yanda ake binne mutun, se suka dawo gida, dasuka dawo gida aduk lokacinda yaron yayi Sallah se yace ALLAH Kaji Qan Mamana!,

 

yaron ya tara kudin wasa, irin takardun da yara ke kira kudi yakai wa malaminsu yace malam nabaka wannan kudi ne don kayiwa mamana Addua!

 

Malam yayi shiru yana jin tausayin wannan yaron yace kabar kudin ka zanyiwa mamanka Addua kyauta, yaro cikin kuka yace Nagode!

 

Yaro Dan Qarami Kenan, Wanda bai mallaki hankalinshi ba! Ina ga kai kuma dake da Hankali???

.

Ya Allah kajiqan Iyayenmu, Ka Gafarta Musu Zunubansu, Ka Sanya Aljannna itace Makomarsu!

 

Don Girman Allah ɗan uwa idan kakaranta katura a groups sabida al’umma su amfana da kai

ALLAHU AKBAR RAYUWA

 

Na saurari bayani mai ratsa zuciya da tsoratarwa game da rayuwa daga bakin Attajirin mai kudi Alhaji Aminu Dantata

 

Wasu ne suka kai masa ziyara gidansa jiya a Kano bayan ya cika shekaru 92 a duniya, a jawabin da yayi yace duk sa’anninsa a Nigeria wadanda ya sani suka taso tare sun mutu, da kyar ne idan mutane 10 da ya sani suna raye

 

Yace yana neman yafiyar kowa, kuma duk wanda ya bata masa ya yafe, yace shi yanzu baya jin dadin rayuwar duniya, fatan mutuwa yakeyi ya cika da imani, da bakinsa ya fadi haka, Jama’a wannan babban darasi ne na rayuwa

 

Alhaji Aminu Dantata attajirin mai kudi ne wanda idan aka tashi lissafa masu kudi a Nigeria dole sai an sanya sunansa, ga kudin ga komai na rayuwa Allah Ya bashi, amma tsufa ya sa ya dena jin dadin rayuwar duniya, yanzu mutuwa da imani kawai yake fata

 

Ga misali da Sarauniyar Ingila Elizabeth, duk abinda take bukata a duniya Allah Ya bata, karshe ta kwanta ta mutu ba tare da jinya ba, kwararrun Likitocin Ingila sukace tsufa ne yayi ajalin rayuwarta

 

To haka fa rayuwar take, idan ka bi Allah Ka zama mutumin kirki idan baka mutu ba dole zaka tsufa, zaka kai matakin da ka dena jin dadin rayuwar duniyar, harcenka ya dena jiye maka dandanon dadin abinci, Kwankwasonka ya gaji balle ka iya sarrafa mace, haka ita ma mace tsufa zai sa ta dena jin sha’awar namiji da komai na rayuwa, ko da tayi tsirara wani namiji ba zai ji sha’awarta ba

 

Haka duk wanda ya zama dan iska ko ta zama ‘yar iska, bata jin magana, ta sa iskanci da karuwanci a gaba, gani take ba zata tsufa ba, to dole sai tsufa yazo ko ba’a mutu ba, kuma karshe dole a mutu, kuma gashi tsufan mutanen banza da na ‘yan iska yafi muni, domin suna koma wa yin kashi da fitsari a kwance su rasa masu wanke musu

 

Babban ribar da mutum zai samu a rayuwa da bayan mutuwa shine bin Allah tare da karfafa zuciya wajen dauriya da hakuri akan kiyaye dokokin Allah, ko da tsufa yazo to za’ayi tsufan alheri da rufin asiri

 

Muna rokon Allah Ya mana muwafaka duniya da lahira, Ya sa mu gama da duniya lafiya da imani

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button